Sirrin Firaqu (Raba Alaqa Da Qauna)

SIRRIN RABA QAUNA, RABA ALAQA, RABA SOYAYYA, RABA MUTANE BIYU KOMAI QARFIN ALAQARDA TAKE TSAKANINSU

 Assalamu alaikum wa rahmatullah ta'ala wa barakaatuh jama'a ƴan uwa maza da mata masu albarka mabiya wannan shafin nawa mai albarka ina gaisheku tare da yiwa kowa fatan alkhairi a duniya da lahira, tare da addu'a Alah ya biyawa kowa buqatunsa na alkhairi, Allah yasa kada mu ci hakkin wani a rayuwa ko mu ci amanar wani amin.

Yau dai na zo da wani aiki abun tsoro wanda ba'a sakin irinsa a internet saboda ɗaukar alhaki ne da irin wannan asirin, domin wasu daga cikin mutane zasu iya cewa su yi amfani da shi ta hanyoyinda basu dace ba, wanda kuma hakan zai janyo shiga haqqin wani, kuma hakan rashin tsoron Allah ne, Allah zai isar masa, amma ana samun masu yin wannan sirri tsakaninsu da Allah tabbas, kamar wanda yake so ya raba alaqa tsakanin qanwarsa dawani saurayinta wanda yake ɗan isa kokuma wanda bashida halin qwarai, kokuma wani wanda yake so ya raba mummunar alaqar da take tsakanin wasu mutane biyu, kokuma ɗan uwan ka ko qanenka yana tare da wasu abokanansa waɗanda suke koya masa abubuwa marar kyau kokuma suke so su ɗorashi akan wata hanya wadda bata dace ba, to ga aikin da za'a yi domin raba alaqa a tsakanin mutanen banza kokuma waɗanda basu dace ba.

Ga yadda ake aikata wannan babban aikin👇

Da farko dai a samu qwai na kaza🥚🐔, bara gurbi kokuma dinge guda 4

Nasan wasu zasu iya cewa menene baragurbi ko dinge, to bara gurbi shine qwai wanda kaza ta kwanta ta qyan qyashe ƴan uwan sa amma shi ta barshi kokuma ta kwantashi amma kuma ta tashi ta daina kwanciyar sa, kuma kaza bata komawa tagama da kwanciyar sa har abada, wanda ya zama waste dai, wanda zaku ji yana wari yana ɗoyi, to shi ake kira dinge, kokuma ake kiran shi bara gurbi,

Ana samun wannan qwan a ko ina inda kaza take kwanciya, kokuma inda kaza tagama qyanqyasa.

Akula :Ka tabbatar da cewa akwai bishiyar kuka a bayan garin ku kokuma a bãkin gari kokuma agefen gari,domin da ita ce za'a qarasa aikin, kuma ba'a amfani da bishiyar cikin gari kokuma ta cikin anguwa, ga misalin hoton bishiyar kukar👇


Cigaban bayani👇
Bayan an samo bara gurbi ko dinge guda 4 sai ayi niyya ayi arwala asamu wuri a zauna da waɗannan bara gurbi guda 4 sai ayi👇

Istigfari qafa 100

Salatin annabi qafa 100

La ilaha illallah qafa 100

Bayan ka gama waɗannan addu'o'i na miftahul amal ɗin, sai ka ɗauki qwai ɗaya daga cikin waɗannan qwai guda 4 ɗin sai kariqe shi a hannun ka kowanne hannu ne (dama ko hagu), sai kafara wuridin Fal fãriqãti farqãã qafa dubu ɗaya (1000) kana yi kana tofawa akan wannan qwan da ka ɗauka, amma duk qafa ɗari idan kazo ɗari sai ka tsaya kace “ALLAH KARABA WÃNE DA WANCE KAMAR YANDA KA RABA SAMA DA QASA, KAMAR YANDA KARABA KARE DA KURA” ka ambaci sunan waɗanda ake so a raba, misali idan Maryam da Aliyu ake so a raba tsakaninsu sai ace “ALLAH KARABA ALIYU DA MARYAM KAMAR YANDA KA RABA SAMA DA QASA KAMAR YANDA KA RSBA KARE DA KURA” sannan kaci gaba, haka zalika in ka qara kaiwa ɗari tagaba sai ka tsaya kace “ALLAH KARABA WÃNE DA WANCE KAMAR YANDA KA RABA SAMA DA QASA KAMAR YANDA KA RSBA KARE DA KURA”, haka zaka dinga yi har sai ka kai dubu ɗaya, shima na dubu ɗaya sai kaa furta wannan kalamin cewa “Allah yaraba wane da wance kamar yanda ya raba kare da kura kamar yanda ya raba sama da qasa”, bayan ka gama dubu ɗaya sai ka ajiye wannan qwan na farko gefe, sai kaɗauki na biyu shima ka karantã masa ayar “Fal Fãriqãti Farqaa” kamar yanda ka yiwa wancan qwan na farko haka zaka yimasa, shima ka ajiye shi a gefe tare da na farkon, haka shima qwai na uku haka zaka yi masa, har kazo kan qwai na huɗu duk haka zaka yimusu, bayan ka kammala gaba ɗaya na qwayaqwayin guda huɗu sai ka tashi kai tsaye, ba'a yin addu'ar komai a gurin, ba'a shafa fatiha, kawai miqewa tsaye zaka yi, sai kaje bayan gari kokuma gefen gari kokuma qarshen gari inda kasan akwai iccen kuka tare da waɗannan qwayaqwayin guda 4, in ka zo gaban wannan iccen kukar sai kaje ɓangaren gabas ka ɗauki qwai ɗaya kace “ALLAH KARABA WÃNE DA WANCE, KAMAR YADDA KARABA KARE DA KURA, KAMAR YADDA KARABA SAMA DA QASA”, sai ka jefa qwan a jikin bishiyar kukar ta ɓangaren gabas, kadawo ɓangaren yamma ma kace “ALLAH KARABA WÃNE DA WANCE, KAMAR YADDA KARABA KARE DA KURA, KAMAR YADDA KARABA SAMA DA QASA” haka zaka yi a ɓangaren arewa da qwai na uku sai ka dawo ɓangaren kudu shima haka zakayi da qwai na qarshe, kowane ɓangare qwai ɗaya zaka jefa masa.

A dai dai Lokacinda zaka jefa qwan a farko wallahi zaka ji wani iri, zakaji yanayin da baka taɓa ji ba wallahi, zaka ji ijaba a jikin ka zaka tabbatar aikine mai qarfi mai ijaba ka yi, kuma in bakada gaskiya cuta kake so kayi wallahi kar kayi, domin abunda yafi sauqi shine kayi haquri, Allah yana son masu haquri Allah zai skaa masu haquri a aljanna ba tareda hisabi ba, in kayi kuma ya kasance wanda kayiwa yanada Dafa'i kai kuma bakada shi wallahi zai iya dawo maka.

Bayan ka kammala wannan aikin sai ka tafiyarka gida ka basu kwana 3 ko 5 kaga ikon Allah yadda za su rabu wlh.

Wannan aikin mujabbani ne, yana aiki sosai, yana tasiri sosai cikin iko da iyawar Allah subhanahu wa ta'ala 

Domin tambaya ko neman qarin bayani ayimun magana a WhatsApp da wannan numbar tawa 08136560680 ko 09020132884, idan bata shiga ba zaku sameni a WhatsApp da numbar a koda yaushe

Aji tsoron Allah,

Idan ba zaka iya taimakon mutum ba, to karka zalunceshi, idan ba zaka iya sa hannu a aljihun ka kaba mutum ba, to karka sakamasa hannu a aljihu kaciro.
Bayan haka ga link na WhatsApp group dinmu: https://chat.whatsapp.com/DfCzfdMbVNQ9adedPhDBLn
Tiktok: 
YouTube Channel: https://youtube.com/@dandalinshehudiezer1819?si=FK_IusL29wplpNAc akwai video yanda akeyin irin wannan ayyuka dayawa achan, kuyimana subscribing kuma kudanna qararrawa


Alhamdulilllah 

Ku kasance tare da ni a koda yaushe, zan dinga kawo muku sirruka da addu'o'i da magunguna domin amfaninku da izinin Allah
Next Post Previous Post
1 Comments
  • Umar kakangi
    Umar kakangi May 1, 2022 at 9:55 AM

    Assalamu Alaikum, don Allah, tambaya ta anan itace, ga wanda akayi wa firraqu kamar mata da miji, wanda bincike ya nuna raba su aka yi, toh shi kuma yaya mutum zai yi domin karya firrakun, Allah ya saka da alkhairi.

Add Comment
comment url